Allah ya kawo mu damuna kuma muna fatan Allah ya sanya al-barka a wannan damunar tamu ta bana. Abun dake faruwa shine mafiya yawa daga manoman mu, suna batun akan chewa wai amfanin noman da sukayi bara baiyi kudiba, ko kuma baiyi tsada ba, shine dalilin dayasa wasu ke cewa bazasu suka abunda suka shukaba bara.
To Amman kuma idan kukayi duba akan abunda suka shuka baran ai baiwuce Masara, Gero, dawa, da shinkafa ba. To Amman kuma suna cewa wai bazasu sake sukawaba a wannar shekarar, sai naga kuma ai wannan abincin sune da idan babushi ake shiga matsar Rayuwa. Kusanifa duk wata damuwa matukar a kwai lafiya,to babu wani abu da mutum ke bukata kamar abinci.
Sanna mafa duk Gwa-gwar mayar mutanen mu na arewa bai wuce akan abunda za'aciba, domin kuwa idan kana da abinci a gidan ka, to sauran al-amuran Rayuwa za'a iya hakuri da wasu. Don haka ba dadai bane ace za'a kaurace wa ban-garen abinci a nausa ban-garen Neman kudi muraran ba.kuma idan har muka koma noman abunda zai kawo kudin ai sai idan Gwamnati tanada yadda zata sarrafa wannan abun da muka noma tukunna zaiyi tsadar ta ake burin akai.
Munan yan Arewa babu wani abu daya dace damu, kuma akasan mu dashi face NOMA DA KIWO. Aima wannan shine martabar mu aduniya baki daya. Idan muna bukatar mu Noma kayan kudi to wannan lallai sai idan Gwamnati ta saka mana hanu acin lamarin, ta hanyar kawo injunan da zasu sarrafa abun da muka Noma,sannan Gwamnati ta bamu kayan noman na zamani, wadanda suka hada da IRIN NOMA,TAKI AKAN LOKACI,DA KUMA TALLAFI. Idan mun samu wadannan to kunga zamu noma abincin mu, zamu noma abunda akeso na kudi.Amman yanzu Gaskiya garajene.
Sabo da yin hakan zaisa mu fuskanci tsadar Rayu, da kuma yinwa a kasa baki daya.kuma talaka shi zaifi kowa shan wahala saboda komai ya faru naga talaka yafi shan wahala. Shawara ta dai anan shine kada mubar abunda muka sani, mutafi neman abunda baya da tabbas.
SANI ABUBAKAR DIKUWA.
08168604297
DAGA: Sani Abubakar Dikuwa. Bismillahirrahmanirrahim, Ina mana maraba da zuwan wata mai alfarma watan Ramadan. Muna Godiya ga Allah SWT da ya tsawaita rayuwar mu zuwa wannan lokaci, Allah Ya karbi Ibadun mu. Bayan Haka, Azumi daya ne daga cikin manyan ibadu a wurin Allah SWT Kaman yanda yazo a Qur’ani da Hadisan Manzon Allah SAW. Ga wasu daga ciki: * Idan watan Ramadaan ya fara, ana rufe kofofin wuta kuma ana bude kofofin Aljannah, kuma ana daure shedanu. [ Bukhari Fat’h 3277] * Azumtan Watan Ramadaan Daya yake da azumtan watanni goma. [Musnad Imam Ahmad, 5/280] * Duk wanda ya azumci watan ramadaan da imani tare da yakinin samun yaddan Allah, za’a gafarta masa dukkan zunuban sa da suka gabata. [Bukhari, GUZURIN7] * Azumi bai da Ibadan da yayi gogayya da shi a lada, kuma ba’a dawo da addu’an mai azumi. [Al-Bukhari, fat’h 1904] * Mai azumi yana da lokuta guda biyu na jin dadi; daya lokacin da yayi buda baki, na biyu kuma lokacin da ya gamu da Ubangijin sa yana murna akan azumin da y...
Allah ya saka
ReplyDelete