Skip to main content

Falalar Azumi.

 DAGA: Sani Abubakar Dikuwa.

Bismillahirrahmanirrahim,

Ina mana maraba da zuwan wata mai alfarma watan Ramadan. Muna Godiya ga Allah SWT da ya tsawaita rayuwar mu zuwa wannan lokaci, Allah Ya karbi Ibadun mu.

Bayan Haka, Azumi daya ne daga cikin manyan ibadu a wurin Allah SWT Kaman yanda yazo a Qur’ani da Hadisan Manzon Allah SAW. Ga wasu daga ciki:

* Idan watan Ramadaan ya fara, ana rufe kofofin wuta kuma ana bude kofofin Aljannah, kuma ana daure shedanu. [ Bukhari Fat’h 3277]

* Azumtan Watan Ramadaan Daya yake da azumtan watanni goma. [Musnad Imam Ahmad, 5/280]

* Duk wanda ya azumci watan ramadaan da imani tare da yakinin samun yaddan Allah, za’a gafarta masa dukkan zunuban sa da suka gabata. [Bukhari, GUZURIN7]

* Azumi bai da Ibadan da yayi gogayya da shi a lada, kuma ba’a dawo da addu’an mai azumi. [Al-Bukhari, fat’h 1904]

* Mai azumi yana da lokuta guda biyu na jin dadi; daya lokacin da yayi buda baki, na biyu kuma lokacin da ya gamu da Ubangijin sa yana murna akan azumin da yayi. [Silsilatul Saheha 1797]

* Azumi zai yi ceto a ranar hisabi inda zai ce: “Ya Ubangiji, na hana shi abincin sa, da abubuwan da yake bukata bayyanannu a lokacin yini, a bar ni in cece shi” [Sahehul Targib, 1/407]

* Warin bakin mai Azumi yafi kamshi a wurin Allah SWT akan turaren Miski [Sahihu Muslim, 2/807]

* Azumi kariya ne da yake nesantar da mutum daga azabar wutan jahannama. [Saheehul Jaami 3880]

* Duk wanda yayi azumi na kwana daya saboda Allah, Allah SWT zai nesantar da fuskar sa tazarar shekaru 70 daga wuta. [Sahihu Muslim 2/808]

* Duk wanda yayi azumi na kwana daya don neman falalan Ubangiji, kafin ya buda baki ya koma zuwa ga Allah, to zai shiga Aljannah [Saheehul Targib 1/412]

* A cikin Aljannah akwai wani kofa mai suna Al’Rayyan, babu wadanda zasu shige ta sai masu azumi. [Sahihul Bukhari 1797]

* A cikin watan Ramadaan ne Allah SWT ya saukar da AlQur’ani, kuma a cikin ta ne daren Lailatul’Qadr yake, wanda Allah SWT yace daren yafi watanni dubu.

* Duk lokacin shan ruwa bayan azumi, Allah yana zaban bayin sa wadanda zai ‘yanta daga wuta. [Saheehul Targhib 1/419].


Sai mun sake haduwa a wani rubutun.

Comments

Popular posts from this blog

NOMAN KIFI

  Yadda ake fara noman kifi A gaskiya ma, bayanin kyau ya bambanta daga mutum zuwa mutum. Duk da haka, idan aka ambaci kwayoyin ruwa musamman kifaye a cikin tafki mai kyau, kowa yana ganin su suna da ban sha'awa. Duk da yake yana iya yin sauti duka hadaddun zuwa raya kifin, a nan, za mu ɗauke ku wannan tsari mataki-mataki don tabbatar da cewa ba kawai kayan aiki ne kawai ba amma har ma da kuzarin fara noman kifi. Cike da sha'awa, goyan bayan gwaninta, muna juyar da duk ra'ayoyinku da zaburarwa zuwa ga nasara mai ban sha'awa. Menene noman kifi? Mahimmanci, noman kifin da aka fi sani da pisciculture tsarin ciyar da halittun da ke zaune a cikin ruwa na kasuwanci ko dai a cikin yanayi mai sarrafawa ko kuma ba a sarrafa shi ba don ƙara yawan aiki. Yadda ake fara noman kifi mataki-mataki Kifin kifin tsari ne sosai. Kamar yadda aka ambata a baya, muna ɗaukar ku da gwaninta tun daga lokacin da kuka zaɓi wurin da kuke son adana kifi har zuwa mataki na ƙarshe inda zaku tallata sh...

FALALAR AZUMI.

FALALAR AZUMIN WATAN RAMADAN Falalar watan azumin Ramadan da irin rahman da ke cikinsa DAGA: Sani Abubakar Dikuwa Azumin Ramadan na da falala da yawa. A cikin wannan wata na Ramada ne aka fara saukar wa da fiyayyen hallita Annabi Muhammadu (S.A.W) da littafi mai tsarki. Saboda tsarkin wannan wata ne ake rufe duk wani shaidani da kofofin gidan wuta sannan a bude kokofin gidan Al-jannah. Daga cikin falalar azumin sun hada da:- 1. Azumin Ramadan na kankare zunubin mutum kamar yadda yazo a hadisin Khuzaifah (R.A.) Yace: Manzon Allah {S.A.W} yace: "Fitinar mutum acikin iyalansa, da dukiyarsa ko makwabcinsa sallah da azumi da sadaka suna kankaresu (Bukhari).” 2. Ya zo a hadisin Abi Umamata (R.A.) yace: "Nacewa Manzon Allah (s.a.w) ka umarceni da wani aiki da Allah Zai amfanar dani dashi sai yace ka lizimci azumi, domin babu kamarsa" (dukkan wadanna hadisai sun tabbata a targhib, tahakikin Sheikh Albani juzu'I na farko shafi na 578). 3. Azumi kuma shine Musababin tsoron All...