Skip to main content

FALALAR AZUMI.

FALALAR AZUMIN WATAN RAMADAN


Falalar watan azumin Ramadan da irin rahman da ke cikinsa


DAGA: Sani Abubakar Dikuwa

Azumin Ramadan na da falala da yawa. A cikin wannan wata na Ramada ne aka fara saukar wa da fiyayyen hallita Annabi Muhammadu (S.A.W) da littafi mai tsarki. Saboda tsarkin wannan wata ne ake rufe duk wani shaidani da kofofin gidan wuta sannan a bude kokofin gidan Al-jannah.


Daga cikin falalar azumin sun hada da:-


1. Azumin Ramadan na kankare zunubin mutum kamar yadda yazo a hadisin Khuzaifah (R.A.) Yace: Manzon Allah {S.A.W} yace: "Fitinar mutum acikin iyalansa, da dukiyarsa ko makwabcinsa sallah da azumi da sadaka suna kankaresu (Bukhari).”


2. Ya zo a hadisin Abi Umamata (R.A.) yace: "Nacewa Manzon Allah (s.a.w) ka umarceni da wani aiki da Allah Zai amfanar dani dashi sai yace ka lizimci azumi, domin babu kamarsa" (dukkan wadanna hadisai sun tabbata a targhib, tahakikin Sheikh Albani juzu'I na farko shafi na 578).


3. Azumi kuma shine Musababin tsoron Allah.


4. A watan Ramadan ana bude kofofin gidan Aljanna, sannan kuma ana kulle kofofin gidan wuta sannan a daure shaidanu kamar yadda ya tabbata a hadisin Abi Huraira. (Kuduba Sahihul Bukhari 1899).


5. Hadisi ya tabbata wanda Imam Tirmizi ya ruwaito cewar Manzon Allah {S.A.W.} yace: "Warin bakin mai azumi yafi kamshi fiye da turaren Al-miski a wurin Allah." Hadisi ne sahihi.


6. Yazo a hadisai da dama cewa: Dukkan aikin Dan Adam nasane Malaikune suke rubuta shi, amma azumi wannan na Allah ne Shi Yake sakawa wanda yayi shi (hadisin ya tabbata acikin targhib wattarhib, juz'I na farko shafi na 75).


Muhadu a wani karon nagode Allah ya karbi ibadah.


Comments

Popular posts from this blog

Falalar Azumi.

 DAGA: Sani Abubakar Dikuwa. Bismillahirrahmanirrahim, Ina mana maraba da zuwan wata mai alfarma watan Ramadan. Muna Godiya ga Allah SWT da ya tsawaita rayuwar mu zuwa wannan lokaci, Allah Ya karbi Ibadun mu. Bayan Haka, Azumi daya ne daga cikin manyan ibadu a wurin Allah SWT Kaman yanda yazo a Qur’ani da Hadisan Manzon Allah SAW. Ga wasu daga ciki: * Idan watan Ramadaan ya fara, ana rufe kofofin wuta kuma ana bude kofofin Aljannah, kuma ana daure shedanu. [ Bukhari Fat’h 3277] * Azumtan Watan Ramadaan Daya yake da azumtan watanni goma. [Musnad Imam Ahmad, 5/280] * Duk wanda ya azumci watan ramadaan da imani tare da yakinin samun yaddan Allah, za’a gafarta masa dukkan zunuban sa da suka gabata. [Bukhari, GUZURIN7] * Azumi bai da Ibadan da yayi gogayya da shi a lada, kuma ba’a dawo da addu’an mai azumi. [Al-Bukhari, fat’h 1904] * Mai azumi yana da lokuta guda biyu na jin dadi; daya lokacin da yayi buda baki, na biyu kuma lokacin da ya gamu da Ubangijin sa yana murna akan azumin da y...

SUNAYEN HAUSAWA DA MA'ANONINSU.KASHI NA DAYA.

TANKO: Yaron da aka haifa bayan mata. KANDE: Yarinyar da aka haifa bayan maza. KILISHI: Yarinyar da aka fara haifa babanta ya samu sarauta. BARAU: Yaron da aka haifa ya rayu, amma an haifa wasu kafin shi ba su rayu ba. SAMBO: Yaron da aka haifa bayan maza da yawa. TALLE: Yaron/yarinya da mahaifiya ta rasu tana gama haihuwa. AUDI: Yaron/yarinyar da mahaifi ya rasu kafin a haife. MIJIN-YAWA: Yaron da aka haifa dukkanin kakannin sa suna raye. DIKKO: Yaron da aka fara haifa (Dan fari). SHEKARAU: Yaron da ya shekara a ciki MAIWADA: Yaron da aka haifa iyaye suna cikin wadata. GAMBO: Yaron/yarinyar da aka haifa bayan tagwaye. CINDO: Yaron/yarinyar da aka haifa da yatsu shida. MARKA: Yarinyar da aka haifa lokacin marka-marka. ALHAJI: Yaron da aka haifa lokacin aikin haji. AZUMI: Yaron/yarinyar da aka haifa lokacin azumi. SARKI: Yaron da aka sama sunan sarki. SUNAYEN NA’URORIN BATURE DA AKA CANZA MASU SUNA ZUWA HAUSA. Ford = Hodi Bedford = Bilhodi Mercedes = Marsandi Peugeot = Fijo Volkswagen =...