Skip to main content

SALLOLIN NAFILA NA WATAN SHABAN.

 WATAN SHA'ABAN:

SALLOLIN DARAREN


SHA'ABAN:

DAREN FARKO:


An karbo daga Manzon (S) ya ce: "Wanda ya yi sallah a daren farko na Sha'aban raka'a (12) a kowace raka'a ya karanta Fatiha (1) Kulhuwa (15) Allah zai rubuta masa ladar ibadar shekara goma sha biyu. kuma za a gafarta masa zunubbansa kamar yadda mahaifiyarsa ta haife shi" (Dhiya'us Saliheen.29). 


SALLAH TA BIYU:

Sallah raka'a (2) kowace raka'a Fatiha (1) Kulhuwa(30) Idan an sallame a ce: Allahummah Haaza Ahdiy Indaka Ila Yaumil Kiyamah".Wanda ya yi wannan sallah. Allah zai kare shi daga tarkon shedan da rundunarsa. kuma ya ba shi ladar Salihan bayi. (Dhiya'u.29).


SALLAH TA UKU:

Sallah raka'a (2) kowace raka'a Fatiha (1) Kulhuwa (11) Wanda ya wannan sallah. Allah zai tsre shi daga sharrin halittun sammai da na kassai. kuma zai gafarta masa zunubbai Subu Saba'in na kaba'irah da ke tsakaninsa da shi Allah.


DARE NA BIYU:

Sallah raka'a (2) kowace raka'a Fatiha (1) Kulhuwa (11) Wanda ya yi wannan  sallah. Allah zai tsare shi daga sharrin halittun sammai da na kassai. kuma zai gafarta masa zunubbai Dubu saba'in na kaba'irah da ke tsakaninsa da shi Allah.


SALLAH TA BIYU:

Sallah raka'a (50) a kowace raka'a Fatiha (1) Kulhuwa (1) Falaki (1) Nasi (1) Allah zai sa Mala'iku su daina rubuta masa zunubi na tsawon shekarar. 


DARE NA UKU: 

Sallah raka'a (2) kowace raka'a a karanta Fatiha (1) Kulhuwa (11) Wanda ya yi wannan sallah Allah zai gafarta masa zunubin kaba'ira (70) kuma ya tunkude masa azabar kabari. 


SALLAH TA BIYU:

Sallah raka'a (2) kowace raka'a Fatiha (1) Kulhuwa (25) Allah zai bude wa wanda ya ui wannan sallah kofofin Aljanna ya rufe masa na wuta.


ADDU'A:

Da asubahin daren uku ga watan Sha'aban ne aka haifi Imam Hussain (AS) dan haka ana son karanta addu'ar nan ta 'As'aluka Bihakkil Mauludi Fiy Hazhal Yaumi' da ke shafi na (33) a 'Dhiya'us Saliheen'. ko shafi na 261 a 'Mafateehul Jinan' don Tawassuli da Imam Hussain (AS) ga samin biyan bukatu. 


DARE NA HUDU:

Sallah raka'a (40) a kowace raka'a Fatiha (1) Kulhuwa (25) Allah zai rubuta wa wanda ya yi wannan sallah ladar shahidai (1000) 


DARE NAa BIYAR:

Sallah raka'a (2) a kowace raka'a Fatiha (1) Kulhuwa (150) bayan an yi sallama sai a yi Salatin Annabi (70) Allah zai biyawa mutum bukatu dubu a duniya da lahira.


SALLAH TA BIYU: 

Manzon Allah (S) ya ce:  "Wanda ya yi Sallah raka'a (2) a daren biyar (na Sha'aban) Ya karanta Fatiha (1) Kulhuwa (500) Wato kowace Raka'a Fatiha (1) Kulhuwa (250) bayan ya sallame  ya yi Salatin Annabi kafa (70) Allah zai biya masa bukatu Dubu a duniya da lahira" (Baladul-Ameen.shafi na 181)


DARE NA SHIDA:

Sallah raka'a (4) kowace raka'a Fatiha (1) Kulhuwa (50) Wanda ya yi wannan Sallah Allah zai rabautar da shi. ya kuma yalwata masa kabari.


DARE NA BAKWAI:

Sallah raka'a (2) a raka'ar farko Fatiha (1) Kulhuwa (100) A raka'ar ta biyu. Fatiha (1) Kursiyyu (100) Wanda ya yi wannan Sallah to zai zamo a cikin Muminai.


SALLAH TA BIYU:

Manzon Allah (S) ya ce: "Wanda ya yi sallah raka'a biyu (a dareb 7 na Sha'aban) a raka'ar farko ya karanta Fatiha (1) Kulhuwa (100) A raka'a ta biyu Fatiha (1) Kursiyyu (1) Allah zai amsa addu'arsa. ya biya masa bukatunsa. Kuma a kowace rana (ta watan) za a rubota masa ladar Shahidi" (Baladul Ameen.182).


DARE NA TAKWAS:

Sallah raka'a (2) Raka'ar farko Fatiha (1) Amanar-Rasulu zuwa karshen sura sau (5) sai Kulhuwa (15) A raka'a ta (2) Fatiha (1) ayar karshe ta suratul kahfi (1) sai Kulhuwa (15) Allah zai gafartawa  Wanda ya yi wannan sallah duk laifukansa. 


DARE NA TARA:

Sallah raka'a (4) a kowace raka'a Fatiha (1) Izaja'a (10) Wanda ya yi wannan Sallah Allah zai haramta namansa daga wuta. ya ba shi ladan shahidai (12)


DARE NA GOMA:

Sallah raka'a (4) a kowace raka'a Fatiha (1) da Ayatal Kursiyyu (1) Inna A'adaina (3) Wanda ya yi wannan sallah Allah zai rubuta masa kyawawan aiki dubu Dari.


DARE NA SHA-DAYA:

Sallah raka'a (8) a kowace raka'a Fatiha(1) Kuliya (10) Wanda ya yi wannan Sallah. Allah zai ba shi a kowacce raka'a dausayi a Aljannah.


DARE NA SHA BIYU:

Sallah raka'a (12) kowace raka'a Fatiha (1) Alhakumu (10) wanda ya yi wannan Sallah. Allah zai ba shi ladar bauta a daren Lailatul kadari.


DARE NA SHA UKU:

Sallah raka'a (2) a kowace raka'a Fatiha (1) Watteeni (1) Allah zai gafarta wa mutum zunubbansa baki daya 

SALLAH TA BIYU:

Sallah raka'a (2) kowace raka'a Fatiha (1) Yaseen (1) Tabara (1) Kulhuwa (1) Wanda ya yi wannan sallah. Allah zai azurta shi da boyayyun sirruka na falalar da ke cikin watannin nan guda uku (wato Rajab. Sha'aban. Ramadan) kuma Allah zai gafarta masa dukkan zunubbansa muddin ba shirka ba ne" (Ikbal fil A'amal)


DARE NA SHA HUDU:

Sallah Raka'a (4) a kowace raka'a Fatiha (1) Wal'asri (5) Wanda ya yi wannan Sallah Allah zai rubuta masa ladar masu sallah tun daga Adamu (AS) har ranar karshe.


SALLAH TA BIYU:

Sallah raka'a (4) kowace raka'a Fatiha (1) Yaseen (1) Tabara(1) Kulhuwa (1) Wanda ya yi wannan sallah. Allah zai azurta shi da boyayyun sirruka na falalar da ke ciki  watannin nan guda uku (wato Rajab. Sha'aban. Ramadan) ku ma Allah zai gafarta masa dukkan zunubbansa muddin ba shirka ba ne.


Daga 

SANI ABUBAKAR DIKUWA.

Comments

Popular posts from this blog

Falalar Azumi.

 DAGA: Sani Abubakar Dikuwa. Bismillahirrahmanirrahim, Ina mana maraba da zuwan wata mai alfarma watan Ramadan. Muna Godiya ga Allah SWT da ya tsawaita rayuwar mu zuwa wannan lokaci, Allah Ya karbi Ibadun mu. Bayan Haka, Azumi daya ne daga cikin manyan ibadu a wurin Allah SWT Kaman yanda yazo a Qur’ani da Hadisan Manzon Allah SAW. Ga wasu daga ciki: * Idan watan Ramadaan ya fara, ana rufe kofofin wuta kuma ana bude kofofin Aljannah, kuma ana daure shedanu. [ Bukhari Fat’h 3277] * Azumtan Watan Ramadaan Daya yake da azumtan watanni goma. [Musnad Imam Ahmad, 5/280] * Duk wanda ya azumci watan ramadaan da imani tare da yakinin samun yaddan Allah, za’a gafarta masa dukkan zunuban sa da suka gabata. [Bukhari, GUZURIN7] * Azumi bai da Ibadan da yayi gogayya da shi a lada, kuma ba’a dawo da addu’an mai azumi. [Al-Bukhari, fat’h 1904] * Mai azumi yana da lokuta guda biyu na jin dadi; daya lokacin da yayi buda baki, na biyu kuma lokacin da ya gamu da Ubangijin sa yana murna akan azumin da y...

FALALAR AZUMI.

FALALAR AZUMIN WATAN RAMADAN Falalar watan azumin Ramadan da irin rahman da ke cikinsa DAGA: Sani Abubakar Dikuwa Azumin Ramadan na da falala da yawa. A cikin wannan wata na Ramada ne aka fara saukar wa da fiyayyen hallita Annabi Muhammadu (S.A.W) da littafi mai tsarki. Saboda tsarkin wannan wata ne ake rufe duk wani shaidani da kofofin gidan wuta sannan a bude kokofin gidan Al-jannah. Daga cikin falalar azumin sun hada da:- 1. Azumin Ramadan na kankare zunubin mutum kamar yadda yazo a hadisin Khuzaifah (R.A.) Yace: Manzon Allah {S.A.W} yace: "Fitinar mutum acikin iyalansa, da dukiyarsa ko makwabcinsa sallah da azumi da sadaka suna kankaresu (Bukhari).” 2. Ya zo a hadisin Abi Umamata (R.A.) yace: "Nacewa Manzon Allah (s.a.w) ka umarceni da wani aiki da Allah Zai amfanar dani dashi sai yace ka lizimci azumi, domin babu kamarsa" (dukkan wadanna hadisai sun tabbata a targhib, tahakikin Sheikh Albani juzu'I na farko shafi na 578). 3. Azumi kuma shine Musababin tsoron All...

ƘWAƘWALWAR ƊAN ADAM KASHI NA BIYU

 Ƙwaƙwalwar ɗan’adam (2) DAGA: SANI ABUBAKAR DIKUWA ‘Yan uwa masu karatu assalam alaikum. Barkan mu da wannan lokaci; barkanmu da sake saduwa a wannan shafi mai albarka, wanda ke kawo mu ku bayanai game da jikin ɗan adam, domin ku fa’idantu, kusan yadda jikinku ke aiki. Barkanmu da Sallah! Fatan Allah ya maimaita mana, Amin. A rubutun da mukayi a baya, na kawo wasu daga cikin baiwar da Ubangijin halittu ya yi wa ƙwaƙwalwar ɗan Adam. Yau kuma in sha Allah za mu ga yadda ƙwaƙwalwar take a siffa, da kuma wasu daga cikin ayyukanta. Ƙwaƙwalwar mutum guda ɗaya ce amma tana da ɓangarori uku. Akwai wadda ta cinye ilahirin ƙoƙon kai, da kuma wadda ke ƙasan ƙeya daidai inda wuya ya hadu da kai ta baya, da kuma wadda take ƙasanta, wadda ta haɗe da laaka dake gadon bayan mutum. Mafi girma daga cikinsu ita ce ta farkon, wadda ta cinye dukkanin ƙoƙon kai. A turance ana kiranta da “cerebrum”. Ita kanta ɓari biyu ce: ɓarin hagu da ɓarin dama. Wasu masanan sun ce aikin da ƙwaƙwalwar dama ta ke yi...