Skip to main content

HAKURI DA JURIYA

Hakuri;wani al-amarine mai matukar tsada musamman ga Wanda bashi da Juriya. Hakuri a rayuwa yana da matukar girma idan har ya kasan ce da yafiya. Mafi yawan tashin hankalin da yake kawo fada tsakanin ma'aurata, rashin hakuri ne. Hakama idan kaga an samu tashin-tashina a gari, to shima ya samo asaline daga rashin hakuri. Haka idan an kaure da yaki tsakanin kasa,da kasa wannan ma rashin Hakuri. Inda ace kowa zai hakura, kuma ya tsaya a matsayin sa da an huta da samun tsaiko a tsakanin al-umma. Talaka ya hakura da talaucin sa, ya gane cewa wannan shine ya dace da jarrabawar sa, daga Allah. Mai Dukiya ya hakura da dukiyar daya samu, ya taimaka wa Wanda bashi dashi,ko kuma na kasa dashi. Mai mulki ya hakura da matsayin sa, Wanda Allah ya bashi, yayi adalci acikin al-umma, kuma ya gode da kimar daya samu a cikin mutane. Malami yayi hakuri ya jure wajen karantar da jama'arsa wajen sanin dokoki, kuma ya jure da matsayin sa na mai hurda da masu koyo. Idan da za'ayi haka da kowa zai fahimci ta inda zai taimaki dan-uwansa, kuma da babu batun rashin godiya, ko kuma Tara dukiyar da bazata amfani mai itaba balle Wanda yake hangen an cuceshine wajen tara wannan dukiyar. Da kowa zai iya yiwa dan-uwansa nasiha kuma ya yarda. Sannan da ansamu cigaba mai dimbin yawa, da karuwar zaman lafiya.
      Allah ka sanya mu, muzama bayin ka masu hakuri, da Juriya.
           Amee
Sani Abubakar Dikuwa
       
 08168604297
 

Comments

Popular posts from this blog

NOMAN KIFI

  Yadda ake fara noman kifi A gaskiya ma, bayanin kyau ya bambanta daga mutum zuwa mutum. Duk da haka, idan aka ambaci kwayoyin ruwa musamman kifaye a cikin tafki mai kyau, kowa yana ganin su suna da ban sha'awa. Duk da yake yana iya yin sauti duka hadaddun zuwa raya kifin, a nan, za mu ɗauke ku wannan tsari mataki-mataki don tabbatar da cewa ba kawai kayan aiki ne kawai ba amma har ma da kuzarin fara noman kifi. Cike da sha'awa, goyan bayan gwaninta, muna juyar da duk ra'ayoyinku da zaburarwa zuwa ga nasara mai ban sha'awa. Menene noman kifi? Mahimmanci, noman kifin da aka fi sani da pisciculture tsarin ciyar da halittun da ke zaune a cikin ruwa na kasuwanci ko dai a cikin yanayi mai sarrafawa ko kuma ba a sarrafa shi ba don ƙara yawan aiki. Yadda ake fara noman kifi mataki-mataki Kifin kifin tsari ne sosai. Kamar yadda aka ambata a baya, muna ɗaukar ku da gwaninta tun daga lokacin da kuka zaɓi wurin da kuke son adana kifi har zuwa mataki na ƙarshe inda zaku tallata sh...

Falalar Azumi.

 DAGA: Sani Abubakar Dikuwa. Bismillahirrahmanirrahim, Ina mana maraba da zuwan wata mai alfarma watan Ramadan. Muna Godiya ga Allah SWT da ya tsawaita rayuwar mu zuwa wannan lokaci, Allah Ya karbi Ibadun mu. Bayan Haka, Azumi daya ne daga cikin manyan ibadu a wurin Allah SWT Kaman yanda yazo a Qur’ani da Hadisan Manzon Allah SAW. Ga wasu daga ciki: * Idan watan Ramadaan ya fara, ana rufe kofofin wuta kuma ana bude kofofin Aljannah, kuma ana daure shedanu. [ Bukhari Fat’h 3277] * Azumtan Watan Ramadaan Daya yake da azumtan watanni goma. [Musnad Imam Ahmad, 5/280] * Duk wanda ya azumci watan ramadaan da imani tare da yakinin samun yaddan Allah, za’a gafarta masa dukkan zunuban sa da suka gabata. [Bukhari, GUZURIN7] * Azumi bai da Ibadan da yayi gogayya da shi a lada, kuma ba’a dawo da addu’an mai azumi. [Al-Bukhari, fat’h 1904] * Mai azumi yana da lokuta guda biyu na jin dadi; daya lokacin da yayi buda baki, na biyu kuma lokacin da ya gamu da Ubangijin sa yana murna akan azumin da y...

FALALAR AZUMI.

FALALAR AZUMIN WATAN RAMADAN Falalar watan azumin Ramadan da irin rahman da ke cikinsa DAGA: Sani Abubakar Dikuwa Azumin Ramadan na da falala da yawa. A cikin wannan wata na Ramada ne aka fara saukar wa da fiyayyen hallita Annabi Muhammadu (S.A.W) da littafi mai tsarki. Saboda tsarkin wannan wata ne ake rufe duk wani shaidani da kofofin gidan wuta sannan a bude kokofin gidan Al-jannah. Daga cikin falalar azumin sun hada da:- 1. Azumin Ramadan na kankare zunubin mutum kamar yadda yazo a hadisin Khuzaifah (R.A.) Yace: Manzon Allah {S.A.W} yace: "Fitinar mutum acikin iyalansa, da dukiyarsa ko makwabcinsa sallah da azumi da sadaka suna kankaresu (Bukhari).” 2. Ya zo a hadisin Abi Umamata (R.A.) yace: "Nacewa Manzon Allah (s.a.w) ka umarceni da wani aiki da Allah Zai amfanar dani dashi sai yace ka lizimci azumi, domin babu kamarsa" (dukkan wadanna hadisai sun tabbata a targhib, tahakikin Sheikh Albani juzu'I na farko shafi na 578). 3. Azumi kuma shine Musababin tsoron All...