Skip to main content

HADIN KAI SIRRIN CI GABAN AL-UMMA

                   Hadin kai Mabudin ci gaban al-umma a kan Matsaloli daban-daban da kuma Cigaban su, kai baki dayama Duniya tana tafiyane a kan asasi na hadin kai. Kananan koramu da suke haduwa a wuri guda sune suke haifar da Babban kogi, ta yadda suke kasan-cewa masu karfi harsu rinka Samar da wutar lantarki, sannan su shayar da manya-manyan filaye na Noma,ta yadda wurare zasu koma kore shar, gwanin ban sha'awa.
                   Hakanan itaciya da ga sassa manya da kanana, kamar rassa da ganye, idan basu samu tushe daga saywa guda daya ba, to da ba za'a iya samun bishiyar ba. Hakanan makaranta da haduwar Malamai, da Dalibai, take cika.Hakanan Run-dunonin Sojoji masu Fada, Wadanda zasuyi nasara kayu nansu ba'arabe yakeba, sannan sun kaucewa duk wani sabani a tsakanin su, kuma suna biyayya ga shugaban su guda, Wanda yasan ya kamata, ta yadda zasu samu hadin kai mai karfin gaske a tsakanin su.
                     Amman waccar Rundunar da ko wanne daya daga cikinsu yake wani abu daban dana dan-uwan sa, tabbas ba tare da wani shakkuba za'aiya yin nasara akan su. To daman ko wacce al-umma idan ta samu kanta da ra'ayi daban-daban, ko kuma rashin biyayya ga shugabannin ta. Amman idan ana son samun nasara da ci gaban wadannan al-umma to lallai a samu wasu daga cikin al-umma, kuma su kasance masu kishin wadannan mutanen, wajen bada shawari na kwarai, domin kasan cewa tare.
                      Sannan duk wadan da suka hada Kansu ba'aiya shiga tsakanin su, kuma rashin tsaron da ake samu yana faruwa ta rashin hadin kai, saboda ta yayane mutum zai dauki makami ya kashe Dan-uwansa, inban da rashin hadin kai da sanin mutuncin Dan-uwansa sa. Idan kun zamo a guri guda to kowa zayyi sha'awar shiga cikin ku domin yasan akwai al-barka a tattare daku, kuma zaku iya cimma duk wata manufa da kuka saka agaban Ku, musamman ma ace kun kasance masu gaskiya, da bin doka.
                        Sabo da haka nake ganin samun hadin kai na al-umma, zai Samar da katon gari mai al-barka, da samun tsaro mai nagarta, da samun kwanciyar hankali ga talakawa, idan talakawan suka zauna lafiya, to shuwagaban ninta zasu zauna lafiya. Muna rokon Allah ya sanya al-khairi da samun hadin kai ga al-umma baki daya.
            
                            DAGA:
               SANI ABUBAKAR DIKUWA
E-mail:    saniabubakardikuwa7@gmail.com
                  08168604297

Comments

Popular posts from this blog

Falalar Azumi.

 DAGA: Sani Abubakar Dikuwa. Bismillahirrahmanirrahim, Ina mana maraba da zuwan wata mai alfarma watan Ramadan. Muna Godiya ga Allah SWT da ya tsawaita rayuwar mu zuwa wannan lokaci, Allah Ya karbi Ibadun mu. Bayan Haka, Azumi daya ne daga cikin manyan ibadu a wurin Allah SWT Kaman yanda yazo a Qur’ani da Hadisan Manzon Allah SAW. Ga wasu daga ciki: * Idan watan Ramadaan ya fara, ana rufe kofofin wuta kuma ana bude kofofin Aljannah, kuma ana daure shedanu. [ Bukhari Fat’h 3277] * Azumtan Watan Ramadaan Daya yake da azumtan watanni goma. [Musnad Imam Ahmad, 5/280] * Duk wanda ya azumci watan ramadaan da imani tare da yakinin samun yaddan Allah, za’a gafarta masa dukkan zunuban sa da suka gabata. [Bukhari, GUZURIN7] * Azumi bai da Ibadan da yayi gogayya da shi a lada, kuma ba’a dawo da addu’an mai azumi. [Al-Bukhari, fat’h 1904] * Mai azumi yana da lokuta guda biyu na jin dadi; daya lokacin da yayi buda baki, na biyu kuma lokacin da ya gamu da Ubangijin sa yana murna akan azumin da y...

FALALAR AZUMI.

FALALAR AZUMIN WATAN RAMADAN Falalar watan azumin Ramadan da irin rahman da ke cikinsa DAGA: Sani Abubakar Dikuwa Azumin Ramadan na da falala da yawa. A cikin wannan wata na Ramada ne aka fara saukar wa da fiyayyen hallita Annabi Muhammadu (S.A.W) da littafi mai tsarki. Saboda tsarkin wannan wata ne ake rufe duk wani shaidani da kofofin gidan wuta sannan a bude kokofin gidan Al-jannah. Daga cikin falalar azumin sun hada da:- 1. Azumin Ramadan na kankare zunubin mutum kamar yadda yazo a hadisin Khuzaifah (R.A.) Yace: Manzon Allah {S.A.W} yace: "Fitinar mutum acikin iyalansa, da dukiyarsa ko makwabcinsa sallah da azumi da sadaka suna kankaresu (Bukhari).” 2. Ya zo a hadisin Abi Umamata (R.A.) yace: "Nacewa Manzon Allah (s.a.w) ka umarceni da wani aiki da Allah Zai amfanar dani dashi sai yace ka lizimci azumi, domin babu kamarsa" (dukkan wadanna hadisai sun tabbata a targhib, tahakikin Sheikh Albani juzu'I na farko shafi na 578). 3. Azumi kuma shine Musababin tsoron All...

ƘWAƘWALWAR ƊAN ADAM KASHI NA BIYU

 Ƙwaƙwalwar ɗan’adam (2) DAGA: SANI ABUBAKAR DIKUWA ‘Yan uwa masu karatu assalam alaikum. Barkan mu da wannan lokaci; barkanmu da sake saduwa a wannan shafi mai albarka, wanda ke kawo mu ku bayanai game da jikin ɗan adam, domin ku fa’idantu, kusan yadda jikinku ke aiki. Barkanmu da Sallah! Fatan Allah ya maimaita mana, Amin. A rubutun da mukayi a baya, na kawo wasu daga cikin baiwar da Ubangijin halittu ya yi wa ƙwaƙwalwar ɗan Adam. Yau kuma in sha Allah za mu ga yadda ƙwaƙwalwar take a siffa, da kuma wasu daga cikin ayyukanta. Ƙwaƙwalwar mutum guda ɗaya ce amma tana da ɓangarori uku. Akwai wadda ta cinye ilahirin ƙoƙon kai, da kuma wadda ke ƙasan ƙeya daidai inda wuya ya hadu da kai ta baya, da kuma wadda take ƙasanta, wadda ta haɗe da laaka dake gadon bayan mutum. Mafi girma daga cikinsu ita ce ta farkon, wadda ta cinye dukkanin ƙoƙon kai. A turance ana kiranta da “cerebrum”. Ita kanta ɓari biyu ce: ɓarin hagu da ɓarin dama. Wasu masanan sun ce aikin da ƙwaƙwalwar dama ta ke yi...