Ko wacce Demokradiya ,ta ko wacce zamani, a ko wacce kasa kuma a ko wacce al-umma, so take ta kusanto da Gwamnati kusa da jama'arta.Haka kuma babban burinta shine ayi dokoki da zasu dace da zamanin mutanen ta, a tsare dokoki bisa gaskiya, wannan ne dalilin fito da salon bawa jama'a damar su kafa jam-iyun siyasa,suyi musu sunaye da suka dace da kudurorin su.
A kafa hukumar zabe mai cin gashin kanta, kowa ya zabi Dan takaran da yaga zai tsaremasa kudurorin sa, na gaskiya.a fafutikar zabe a fito da katin jefa kuri'a, wani lokaci kuma ayi yar tinke,domin tan-tance Wanda yayi nasara.kuma koda da kuri'a daya akafika to ka fadi. Saidai ba da sunan mutum mai gaskiya ake bawa hukumar zabe sunayen yan takara ba. Sunan gaskiya baro-baro baya daga cikin abubuwan da za'a tan-tance Dan takara akansu.
A ganina da dai an zabi masu gaskiya, su nemo mafi gaskiya a cikin su.domin ya shugabanci al-umma, irin yadda Sarki yake yi a zaben shuwagaban sa na gar-gajiya,da babu batun ta zarce, ko ta lan-kwashe, da sauya sheka daga wannan jam-iyar zuwa wata jam-yar bata tasoba.A ganina Shugabanci na Dottawa ne, su sukafi kowa kusa da gaskiya. Idan an bawa dottawa zabo dottijo a cikin su domin ayi aikin dottaku, da babu sauran aikin haya gaga.
Amman a yau an hada mashaya, da tsofaffin masu laifi,da fitattun marasa kunya, da sanannun maciya Amana, da gogaggun makaryata, da dakikan mutane, ace wai su zabo Shugaba.kaga anyi zagege kenan inji Dan Fulani daya fado daga bishiyar dabino ya zarce rijiya. Amman wa yafi gaskiya sanin gaskiya, ai matar aure tasan mijin ta ko a cikin daji ta ganshi ,komai taron maza tana iya bam-banceshi. Tabbas da kin gaskiya sai bats.
To Amman anya Demokradiyar mu batashiga wannan halin kuwa. Allah ya kyauta.
Sani Abubakar Dikuwa
08168604297
DAGA: Sani Abubakar Dikuwa. Bismillahirrahmanirrahim, Ina mana maraba da zuwan wata mai alfarma watan Ramadan. Muna Godiya ga Allah SWT da ya tsawaita rayuwar mu zuwa wannan lokaci, Allah Ya karbi Ibadun mu. Bayan Haka, Azumi daya ne daga cikin manyan ibadu a wurin Allah SWT Kaman yanda yazo a Qur’ani da Hadisan Manzon Allah SAW. Ga wasu daga ciki: * Idan watan Ramadaan ya fara, ana rufe kofofin wuta kuma ana bude kofofin Aljannah, kuma ana daure shedanu. [ Bukhari Fat’h 3277] * Azumtan Watan Ramadaan Daya yake da azumtan watanni goma. [Musnad Imam Ahmad, 5/280] * Duk wanda ya azumci watan ramadaan da imani tare da yakinin samun yaddan Allah, za’a gafarta masa dukkan zunuban sa da suka gabata. [Bukhari, GUZURIN7] * Azumi bai da Ibadan da yayi gogayya da shi a lada, kuma ba’a dawo da addu’an mai azumi. [Al-Bukhari, fat’h 1904] * Mai azumi yana da lokuta guda biyu na jin dadi; daya lokacin da yayi buda baki, na biyu kuma lokacin da ya gamu da Ubangijin sa yana murna akan azumin da y...
Comments
Post a Comment