Skip to main content

DANNIYA KO ADALCI, GA YAN SHI'A

                     Sheikh Ibrahim zakzaky ne ya kafa kungiyar shi"a ta kasa, wato IMN a arewacin kasar a birnin Zaria dake a jihar Kaduna a shekar 1980 da 1990. Ya samu wannan hurumi ne ta kwaikwayo da yabo ga juyin juyahalin kasar Iran a 1979 tare da mu'amala da hotunan Ayatullah Ruhollah Khomeini da Ayatullah Ali khamenei a shafinsa na yanar gizo. IMN na kuma goyon bayan kafa gwamnatin Islama a Nigeria. IMN ta dade da kasancewa a bar lura wajen rikici ga gwamnatin Nigeria, wadda ta aiyana IMN a zaman kungiyar rikici tare da anfani domin danne mabiya IMN da duk wani auyukan ta.
                       Sama da shekara goma tun sanda a ka dakile kungiyar IMN--kisan gilla, tare da binne mabiya IMN 347 da hukumar sojojin Nigeria sukayi. A Disamba 2015 a Zaria-kuma duk da cewa COL a jihar Kaduna a 2016 sun dora alhakin a kan sojoji da kuma shawartar cewa a gurfanar da wadanda suka aikata laifin, Amman babu wani jami'in soja da aka kama domin yin bayani.
                      A 2018 yan sandan Nigeria sun cigaba da tsare fitaccen malamin su, sheikh zakzaky, da matar sa malam zeenah Ibrahim, wadan da ake rike dasu batare da gurfanar da su ba, tun Disamba 2015, duk da cewa babbar kotun tarayyar Nigeria a abuja tayi Ummarni a ranar 2-12-2016, cewa a sake su tsakanin kwana 45. Hukomomi kuma sun kama a kalla mabiya IMN 15 a 2018.
                        Gabadaya 2018, mabiya IMN sunyi zanzanga a fadin kasar suna bukatar a saki sheikh zakzaky. A Kaduna da sokoto hukomomin jihohin sun haramta IMN tare da Ibadun su. Kafar labarum IMN na nuni da cewa wasu lokuta ana anfani da tsananin karfi domin domin tarwatsa zanzanga, Wanda ke jawo raunuka da mutuwa a wani lokaci.
                         Tsakanin Oktoba 28, da Nuwamba 1,Musulmai yan Shi'a sunyi tattakin a fadin kasar domin gudanar da Arbaeen-wani bikin addini na Shekara-shekara da yan musulmai, yan Shi'a ke gudanarwa a fadin duniya baki daya domin tunawa da mutuwar Imam Hussein a karni na bakwai. Daruruwan yan Shi'a sunyi tattaki a abuja domin girmama bikin da kuma zanzangar sakin sheikh zakzaky. Kodayake sojojin Nigeria sunce masu zanzangar sun jefi jami'an tsaron Nigeria da duwatsu a abujan.
                       Babu wata shedar dake nuna tashin hankali a tare da mabiya IMN. Sojojin Nigeria sunyi harbe-harbe a cikin jama'a inda suka kashe a kalla mutane 45,kamar yadda kungiyoyin kare hakkin Dan-Adam suka fada. Babu wani jawabi daga gwamnatin Nigeria dake aibata abun da sojojin ta suka aikata akan Wannan anfani da tsananin karfi a kan masu zanzangar lumana. Da farko hukomomi sojojin Nigeria ta aika da sakon Twitter tana mai kare abinda sojojin ta suka aikata,daga baya kuma ta share sakon Twitter data rubuta.
                      To abunda mukeso mu hanga anan shine, ya kamata hukomomin Nigeria idan zasu dauki mataki akan al-ummar kasa, to ta dauki matakin da kowa zai tayata wajen kokarinta, da kuma daukar darassi ga wasu masu son sunyi irin wannan laifin idan har laifine daya shafi kasa bakidaya,ko kuma kwantar da yarzomar da ta taso a cikin kasa. Sannan kuma su dauki duk yan-kasa amatsayin yan-Nigeria wajen yanke hukunci.
                       Sannan su kuma yan-uwa yan kasa bakidaya ya kamata mugane cewa kowacce kasa tana da nata dokokin daya zama dole abisu musamman ma al-amarin tsaro, kuma idan har zamu zama masu tayar da hankalin kasar mu tofa babu batun cigaba, sabo da kullum shuwagabannin mu, suna fama da matsalar tayaya zasu kwantar da tarzomar da muka tayar a cikin kasa.
                         Yanzu idan kun duba abun da yafaru da su yan-uwa yan Shi'a, ai abun bai kamata ba  ace ana kashe yara, mata, da wasu matasan mu na kasa. Wanda muke fatan suzamo manyan gobe, sai gashi a yau suna rasa rayukan su. Sannan itama gwamnatin Nigeria da yakata ta duba abun dake faruwa a wata fuskar, tagane cewa wadannan mutanen suna fafutikar sune akan abunda sukayi imani dashi a addinan ce. Idan kuma akace wannan addinine to yana da wahala ka iya juya tunanin su akai.
                         Saboda haka jama'a da dama sun bayar da shawarar a saki malamin nasu, sannan akafa masa wasu dokokin da ake ganin ya takasu a baya.kuma ya kamata  a gujewa duk wani tashin hankalin da yake haifar da asarar dukiya, da rayukan yan kasa. Sannan kuma a kiyaye duk wata doka da ta bayar da damar kowa yayi addinin sa yadda ya kamata, sannan sai ayi dokar yada addinin ta yadda baza'a samu wasu masu dora matasan mu akan wani al-amari mai kama da son zuciya ba.

       Alhamdulillahi. Nan zamu tsaya sai wani mako zamu cigaba daga inda muka tsaya.
  
                  Sani Abubakar Dikuwa
                            08168604297
        

Comments

Popular posts from this blog

Falalar Azumi.

 DAGA: Sani Abubakar Dikuwa. Bismillahirrahmanirrahim, Ina mana maraba da zuwan wata mai alfarma watan Ramadan. Muna Godiya ga Allah SWT da ya tsawaita rayuwar mu zuwa wannan lokaci, Allah Ya karbi Ibadun mu. Bayan Haka, Azumi daya ne daga cikin manyan ibadu a wurin Allah SWT Kaman yanda yazo a Qur’ani da Hadisan Manzon Allah SAW. Ga wasu daga ciki: * Idan watan Ramadaan ya fara, ana rufe kofofin wuta kuma ana bude kofofin Aljannah, kuma ana daure shedanu. [ Bukhari Fat’h 3277] * Azumtan Watan Ramadaan Daya yake da azumtan watanni goma. [Musnad Imam Ahmad, 5/280] * Duk wanda ya azumci watan ramadaan da imani tare da yakinin samun yaddan Allah, za’a gafarta masa dukkan zunuban sa da suka gabata. [Bukhari, GUZURIN7] * Azumi bai da Ibadan da yayi gogayya da shi a lada, kuma ba’a dawo da addu’an mai azumi. [Al-Bukhari, fat’h 1904] * Mai azumi yana da lokuta guda biyu na jin dadi; daya lokacin da yayi buda baki, na biyu kuma lokacin da ya gamu da Ubangijin sa yana murna akan azumin da y...

FALALAR AZUMI.

FALALAR AZUMIN WATAN RAMADAN Falalar watan azumin Ramadan da irin rahman da ke cikinsa DAGA: Sani Abubakar Dikuwa Azumin Ramadan na da falala da yawa. A cikin wannan wata na Ramada ne aka fara saukar wa da fiyayyen hallita Annabi Muhammadu (S.A.W) da littafi mai tsarki. Saboda tsarkin wannan wata ne ake rufe duk wani shaidani da kofofin gidan wuta sannan a bude kokofin gidan Al-jannah. Daga cikin falalar azumin sun hada da:- 1. Azumin Ramadan na kankare zunubin mutum kamar yadda yazo a hadisin Khuzaifah (R.A.) Yace: Manzon Allah {S.A.W} yace: "Fitinar mutum acikin iyalansa, da dukiyarsa ko makwabcinsa sallah da azumi da sadaka suna kankaresu (Bukhari).” 2. Ya zo a hadisin Abi Umamata (R.A.) yace: "Nacewa Manzon Allah (s.a.w) ka umarceni da wani aiki da Allah Zai amfanar dani dashi sai yace ka lizimci azumi, domin babu kamarsa" (dukkan wadanna hadisai sun tabbata a targhib, tahakikin Sheikh Albani juzu'I na farko shafi na 578). 3. Azumi kuma shine Musababin tsoron All...

ƘWAƘWALWAR ƊAN ADAM KASHI NA BIYU

 Ƙwaƙwalwar ɗan’adam (2) DAGA: SANI ABUBAKAR DIKUWA ‘Yan uwa masu karatu assalam alaikum. Barkan mu da wannan lokaci; barkanmu da sake saduwa a wannan shafi mai albarka, wanda ke kawo mu ku bayanai game da jikin ɗan adam, domin ku fa’idantu, kusan yadda jikinku ke aiki. Barkanmu da Sallah! Fatan Allah ya maimaita mana, Amin. A rubutun da mukayi a baya, na kawo wasu daga cikin baiwar da Ubangijin halittu ya yi wa ƙwaƙwalwar ɗan Adam. Yau kuma in sha Allah za mu ga yadda ƙwaƙwalwar take a siffa, da kuma wasu daga cikin ayyukanta. Ƙwaƙwalwar mutum guda ɗaya ce amma tana da ɓangarori uku. Akwai wadda ta cinye ilahirin ƙoƙon kai, da kuma wadda ke ƙasan ƙeya daidai inda wuya ya hadu da kai ta baya, da kuma wadda take ƙasanta, wadda ta haɗe da laaka dake gadon bayan mutum. Mafi girma daga cikinsu ita ce ta farkon, wadda ta cinye dukkanin ƙoƙon kai. A turance ana kiranta da “cerebrum”. Ita kanta ɓari biyu ce: ɓarin hagu da ɓarin dama. Wasu masanan sun ce aikin da ƙwaƙwalwar dama ta ke yi...